Duk mutumin da yake ganin Hadithi zato ne; zato irin na harshen Hausa sai ya shirya wa barin irin sallar da yake yi a yanzu; sallar da kusan kashi casa’inta cikin dari an ɗauko shi ne daga Hadithi ba wai daga Alƙur’ani ba.
Sai ya shirya wa barin karanta Iƙama, da barin karanta Kabbarar Harama, da barin karanta addu’ar buɗe Salla, da barin karanta sauran kabbarorin cikin Salla, da barin karanta Sami’allahu Liman Hamidah, da barin karanta Rabbana Walakal Hamd, da barin karanta Tasbihi a cikin Ruku’u, da barin karanta Tasbihi a cikin sujuda, da barin karanta Tahiya, da barin karanta Salatin Annabi, da barin karanta Sallama, da barin sunkuyawa da kama guiwa, da barin ɗagawa bayan sunkuyawa, da barin sanya goshi a ƙasa har sau biyu cikin ko wace raka’a, da barin ɗagawa bayan sanya goshi a ƙasa, da barin yin raka’a biyu a sallar Asuba, da barin yin raka’a uku a sallar magariba, da barin yin raka’a huɗu huɗu a sallolin Azahar da La’asar da aisha.